Jam’iyyar PDP bangaren Kabiru Turaki (SAN) ta shigar da ƙara a Kotun Tarayya da ke Abuja, tana neman umarni da zai tilasta wa ’yan sanda su buɗe tare da ficewa daga sakatariyar ƙasa ta jam’iyyar da ke Wadata Plaza.
An rufe sakatariyar ne tun watan Nuwamba bayan rikici tsakanin bangaren Turaki da bangaren da ke goyon bayan Ministan FCT, Nyesom Wike, sakamakon shirya taruka a rana guda, lamarin da ya janyo tsoma bakin ’yan sanda da kulle ginin.
Bangaren Turaki ya ce kullen ya hana shugabancin jam’iyyar gudanar da ayyukanta, inda suke roƙon kotu ta umarci ’yan sanda su cire shingaye tare da hana su sake kulle ofisoshin PDP a Abuja da jihohi 36 har sai an yanke hukunci.



