DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wasu sauye-sauye a dokokin haraji – Gwamnatin Nijeriya

-

Gwamnatin Nijeriya ta jaddada cewa salo guda ɗaya ne kacal sahihi na sabbin dokokin gyaran haraji da aka rattaba wa hannu, tare da musanta zargin cewa an sauya dokokin bayan Majalisar Tarayya ta amince da su.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya bayyana haka a taron manema labarai na ƙarshen shekara da aka gudanar an Abuja.

Google search engine

Ministan ya ce dokokin sun bi dukkan matakan doka a Majalisar Tarayya kafin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba musu hannu, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da su kamar yadda aka tsara. Sai dai ya ce Majalisar Tarayya na duba koken da aka shigar game da zargin bambanci tsakanin abin da aka amince da shi da abin da aka wallafa a mujallar gwamnati.

Rigimar ta biyo bayan korafin dan Majalisar Wakilai Abdussamad Dasuki na Kebbe/Tambuwal, wanda ya ce akwai wasu sashe a dokokin da ba a tattauna ba amma aka saka su. Duk da sukar da wasu ‘yan siyasa suka yi, ciki har da Atiku Abubakar da Peter Obi, gwamnati ta ce dokokin za su fara aiki daga 1 ga Janairu, 2026, yayin da shugaban kwamitin gyaran haraji na fadar shugaban ƙasa, Taiwo Oyedele, ya ce jinkirta aiwatarwa na iya jefa Nijeriya cikin matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wadanda suka yi garkuwa da ‘yan Mauludi 28 a jihar Plateau na neman kudin fansa N1.5m kan kowane mutum

‘Yan bindiga da ake zargin sace mutane 28 a ƙauyen Zak, karamar hukumar Wase, Bashar, jihar Filato, sun tuntubi iyalan wadanda suka yi garkuwa da...

Kungiyar Lauyoyi ta Nijeriya ta bukaci gwamnatin tarayya ta dakatar da aiwatar dokokin haraji

Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta dakatar da aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai cewa rikice-rikicen da suka...

Mafi Shahara