DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon Sakataren kudi na PDP na kasa ya fice daga jam’iyyar

-

Tsohon Shugaban Matasa na Ƙasa kuma Sakataren Kuɗi na Jam’iyyar PDP, Rt. Hon. Abdullahi Hussaini MaiBasira, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar.

MaiBasira ya bayyana hakan ne a wata wasiƙar murabus mai ɗauke da kwanan wata 22 ga Disamba, wadda ya aike wa shugaban jam’iyyar PDP na mazabarsa ta Tudun Wada ta Kudu, Karamar Hukumar Chanchaga a Jihar Neja, inda ya ce murabus ɗin ya fara aiki nan take.

Google search engine

A cikin wasiƙar, MaiBasira ya nuna godiya ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi ya yi aiki a matakai daban-daban tsawon shekaru, yana mai bayyana shawarar barin PDP a matsayin mai matuƙar wahala. Duk da haka, bai fayyace dalilin murabus ɗin ba, sai dai ya ambaci abin da ya kira “yanayi bayyanannu da matsin lamba na zahiri” a cikin jam’iyyar.

Ficewar tasa na da tasiri a siyasar PDP a Jihar Neja, la’akari da rawar da ya taka a harkokin matasa da tsare-tsaren jam’iyya a matakin jiha da ƙasa.

Ko da yake bai bayyana inda zai dosa ba, majiyoyi daga jam’iyyar na hasashen cewa MaiBasira na iya komawa Jam’iyyar ADC, musamman ganin alaƙarsa da goyon bayan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kungiyar Lauyoyi ta Nijeriya ta bukaci gwamnatin tarayya ta dakatar da aiwatar dokokin haraji

Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta dakatar da aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai cewa rikice-rikicen da suka...

Babu wasu sauye-sauye a dokokin haraji – Gwamnatin Nijeriya

Gwamnatin Nijeriya ta jaddada cewa salo guda ɗaya ne kacal sahihi na sabbin dokokin gyaran haraji da aka rattaba wa hannu, tare da musanta zargin...

Mafi Shahara