DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanata Ndume ya bukaci bincike da dakatar da dokokin haraji saboda zargin sauyin da ke ciki

-

Sanata Ali Ndume ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya dakatar da aiwatar da sabbin dokokin sauya haraji da aka tsara fara aiki a watan Janairu, sakamakon ce-ce-ku-ce kan yadda aka tsara dokokin bayan amincewar Majalisar Tarayya.

Ndume ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba a Abuja, inda ya ja hankalin gwamnati kan rahotannin da ke nuna cewa an canza wasu sassa na dokokin bayan amincewa da su.

Google search engine

Hakazalika ya yi kira ga Shugaba Tinubu da ya kafa kwamitin bincike na musamman domin tantance gaskiyar dokokin da kuma gano sahihancin zargin canje-canjen kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sanatan ya gargadi cewa fara aiwatar da dokokin ba tare da warware zarge-zargen ba zai iya haifar da matsalar inganci da rage amincewar jama’a ga dokokin gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Akwai bukatar dole sai ‘yan kwallon Super Eagles sun inganta wasansu matukar suna son nasara – Eric Chelle

Kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya bayyana cewa har yanzu Nijeriya na da damar ingantawa a gasar Cin Kofin Afirka ta 2025 duk da nasarar...

Mafi Shahara