DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanata Ndume ya bukaci bincike da dakatar da dokokin haraji saboda zargin sauyin da ke ciki

-

Sanata Ali Ndume ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya dakatar da aiwatar da sabbin dokokin sauya haraji da aka tsara fara aiki a watan Janairu, sakamakon ce-ce-ku-ce kan yadda aka tsara dokokin bayan amincewar Majalisar Tarayya.

Ndume ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba a Abuja, inda ya ja hankalin gwamnati kan rahotannin da ke nuna cewa an canza wasu sassa na dokokin bayan amincewa da su.

Google search engine

Hakazalika ya yi kira ga Shugaba Tinubu da ya kafa kwamitin bincike na musamman domin tantance gaskiyar dokokin da kuma gano sahihancin zargin canje-canjen kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sanatan ya gargadi cewa fara aiwatar da dokokin ba tare da warware zarge-zargen ba zai iya haifar da matsalar inganci da rage amincewar jama’a ga dokokin gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara