DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya yi ma Tinubu alkawarin rike masa PDP don kar su ba shi matsala a zaben 2027 – Seyi Makinde

-

Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya ce saɓanin da ke tsakaninsa da Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya samo asali ne daga furucin Wike na cewa zai “riƙe PDP” domin taimaka wa Shugaba Bola Tinubu sake cin zaɓe a 2027.

Makinde ya bayyana hakan ne a wata hira da manema labarai a Ibadan, inda ya ce ya yi mamaki lokacin da Wike ya faɗi hakan a gaban Shugaba Tinubu, alhali shugaban Nijeriyar bai nema ba kuma bai amince da hakan ba. Ya ce Wike na da ’yancin goyon bayan Tinubu, amma bai kamata ya hana sauran ’yan PDP kare jam’iyyar da dimokuraɗiyya ba.

Google search engine

Sai dai mai taimaka wa Wike kan harkokin yaɗa labarai, Lere Olayinka, ya caccaki Makinde, yana cewa gwamnan Oyo mutum ne mai bin son zuciyarsa kawai ba tare da biyayya ga jam’iyya ko mutum ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Olayinka ya zargi Makinde da sauya jam’iyya sau da dama saboda muradin kansa, yana mai cewa bayan zaɓen 2027 ma, Makinde zai sake ficewa daga PDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara