DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya yi ma Tinubu alkawarin rike masa PDP don kar su ba shi matsala a zaben 2027 – Seyi Makinde

-

Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya ce saɓanin da ke tsakaninsa da Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya samo asali ne daga furucin Wike na cewa zai “riƙe PDP” domin taimaka wa Shugaba Bola Tinubu sake cin zaɓe a 2027.

Makinde ya bayyana hakan ne a wata hira da manema labarai a Ibadan, inda ya ce ya yi mamaki lokacin da Wike ya faɗi hakan a gaban Shugaba Tinubu, alhali shugaban Nijeriyar bai nema ba kuma bai amince da hakan ba. Ya ce Wike na da ’yancin goyon bayan Tinubu, amma bai kamata ya hana sauran ’yan PDP kare jam’iyyar da dimokuraɗiyya ba.

Google search engine

Sai dai mai taimaka wa Wike kan harkokin yaɗa labarai, Lere Olayinka, ya caccaki Makinde, yana cewa gwamnan Oyo mutum ne mai bin son zuciyarsa kawai ba tare da biyayya ga jam’iyya ko mutum ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Olayinka ya zargi Makinde da sauya jam’iyya sau da dama saboda muradin kansa, yana mai cewa bayan zaɓen 2027 ma, Makinde zai sake ficewa daga PDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku ya soki gwamnatin Tinubu kan zargin kin bin umurnin kotun koli na ba kananan hukumomi kudadensu kai tsaye

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke jinkirta aiwatar da hukuncin Kotun Koli da...

‘Yan sanda sun cafke wata daliba ‘yar Nijeriya da ta boye hodar iblis a cikin biredi a Indiya

Masu binciken manyan laifuka (Central Crime Branch) a ƙasar Indiya sun cafke wata ’yar Nijeriya mai shekara 29, Olajide Esther Iyanuoluwa, bisa zargin safarar hodar...

Mafi Shahara