DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Cin hanci da rashawa na boye irin albarkar da Allah Ya ajiye a Nijeriya in ji shugaban hukumar EFCC

-

Shugaban Hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce cin hanci da rashawa na boye albarkar da Allah Ya yi wa Nijeriya tare da hana ƙasar cimma cikakken ci-gabanta.

Olukoyede ya bayyana hakan ne a Abuja a ranar Laraba yayin saƙon Kirsimetinsa ga ’yan Nijeriya, inda ya yi kira da a haɗa kai wajen yaƙar cin hanci da rashawa domin ƙasar ta samu ƙarfi da wadata. Ya ce cin hanci na daga cikin manyan matsalolin da ke hana albarkar rayuwa da Allah Ya tanadar wa ƙasa.

Google search engine

Ya kuma bukaci ’yan Nijeriya su rungumi ƙimomin da Annabi Isa (AS) ya koyar na soyayya, haske da fata yana mai cewa su ne ginshiƙan ciyar da ƙasa gaba.

Shugaban EFCC ya ƙara da kira ga jama’a su goyi bayan ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Tinubu, yana mai cewa hakan zai ƙarfafa fata da amincewa cewa Nijeriya za ta iya shawo kan ƙalubalen da ke gabanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya umurci karin jami’an tsaro a jihar Borno biyo bayan harin da aka kai a masallaci – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin rundunonin tsaro na musamman zuwa Maiduguri, Jihar Borno, domin kamo waɗanda suka kai...

Kungiyar kwadago ta bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da dokokin harajin da aka gurbata

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta bukaci ’yan Nijeriya da su ƙi duk wata dokar haraji da aka ce an sauya ko an yi mata...

Mafi Shahara