DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Arewacin Nijeriya sun yi tir da harin da aka kai masallaci a Maiduguri

-

Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewacin Nijeriya ta yi kakkausar suka kan harin kunar bakin wake da aka kai Masallacin Kasuwar Gomboru a Maiduguri, Jihar Borno, inda ta bayyana harin a matsayin dabbanci, rashin imani da kuma yunƙurin tada tsoro da rushe zaman lafiya.

Shugaban kungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya mika ta’aziyyarsa ga gwamnatin Borno da Gwamna Babagana Umara Zulum, da iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata.

Google search engine

Yahaya ya ce kai hari wurin ibada babban laifi ne ga tunanin ɗan Adam da tsarkin addini, yana mai jaddada cewa irin wadannan hare-hare ba za su karya gwiwar Arewa ba, illa ma su kara dankon zumunci wajen yakar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi.

Hakazalika ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da shugabannin Borno da kada su karaya, tare da bukatar a kara tsaurara tsaro musamman a wuraren ibada da tarukan jama’a, musamman a lokutan bukukuwa, domin hana aukuwar irin wannan hari a gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take...

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin...

Mafi Shahara