DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu bai sauya Femi Gbajabiamila daga mukamin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa ba – Bayo Onanuga

-

Fadar Shugaban Nijeriya ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Shugaban Ma’aikatansa, Hon. Femi Gbajabiamila, da Sakatarensa, Hakeem Muri-Okunola.

A wata sanarwa da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar 25 ga Disamba, ya ce labarin ƙarya ne tsagwaronsa, inda ya jaddada cewa Gbajabiamila na nan daram a kan muƙaminsa.

Google search engine

Sanarwar ta ƙara da cewa Hakeem Muri-Okunola ma yana nan a matsayinsa na “Principal Private Secretary”, tana mai kira ga ’yan Nijeriya da su yi watsi da labaran bogi, tare da gargaɗin kafafen yaɗa labarai su rika tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara