DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sandan Nijeriya sun kama wani da ya tsere daga gidan gyaran hali da wasu masu manyan laifuka a wani samame mabambanta a fadin kasar

-

Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta ce rundunarta ta musamman (STS) ta kama wani fursuna da ya tsere daga gidan gyaran hali da kuma wasu mutane 21 a jihohi daban-daban bisa zargin fashi da makami, garkuwa da mutane, satar shanu, satar mota, safarar miyagun ƙwayoyi da kwaikwayon jami’an tsaro.

Mai magana da yawun rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya ce an kai samamen ne bisa sahihan bayanan sirri, inda aka ƙwato bindigogi shida ciki har da AK-47, AK-49 da LAR, tare da harsasai, motoci, babura da sauran kayayyakin laifi.

Google search engine

A cewarsa, daga cikin wadanda aka kama har da Ayo Abiodun, fursunan Kuje da ya tsere, da ake zargi da fashin wani jami’in soja, da kuma wasu mutane da ke da alaƙa da ’yan fashi da masu garkuwa da mutane a Kaduna, Abuja, Lagos, Ogun, Edo da Nasarawa.

Hundeyin ya ƙara da cewa bincike na ci-gaba, kuma za a gurfanar da dukkan waɗanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike, yana mai jaddada kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Kano ta haramta biyan haraji da tsabar kudi daga 1 ga watan Janairu

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da cewa daga 1 ga Janairu, 2026, ba za a amince da biyan haraji da tsabar kuɗi ko takardar banki...

Shugaba Tinubu ya umurci karin jami’an tsaro a jihar Borno biyo bayan harin da aka kai a masallaci – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin rundunonin tsaro na musamman zuwa Maiduguri, Jihar Borno, domin kamo waɗanda suka kai...

Mafi Shahara