DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun ceto wani mutum da shanu a tsakanin Kano da Katsina

-

Sojojin rundunar haɗin gwiwa na Joint Task Force sun yi nasarar ceto wani mutum da aka sace tare da kwato wasu shanu da ‘yan bindiga suka kwace, bayan artabu da suka yi da su a iyakar jihohin Kano da Katsina.

Rahotanni daga rundunar sojin sun nuna cewa lamarin ya faru ne a safiyar Lahadi a yankin Yankwada na jihar Kano, bayan sojoji sun samu bayanan sirri kan motsin wasu ‘yan bindiga da ke shigowa daga yankunan Daurawa da Kira na jihar Katsina zuwa bangaren Kano.

Google search engine

Majiyoyin sojin sun bayyana cewa dakarun sun tare ‘yan bindigar ne a yankin Ungwan Dogo da Ungwan Tudu, inda aka yi musayar wuta mai zafi tsakaninsu.

A yayin artabun, an samu nasarar ceto wani mutum mai suna Rabiu Alhaji Halilu, mai shekaru 38, wanda aka sace,sai dai rahotanni sun ce an harbi Halilu da bindiga a kafa, inda aka gaggauta kai shi asibitin na soji da ke Faruruwa domin samun kulawar likitoci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dokokin Taraba ta musanta cewa Kakakinta ya raba Naira 1000 a matsayin barka da Kirsimeti

Majalisar Dokokin Jihar Taraba tare da Zing Watch Group sun musanta rahotannin da ke yawo cewa Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Taraba, John Bonzena, ya raba...

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai yi balaguro zuwa Turai

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bar birnin Lagos a ranar Lahadi, 28 ga Disamba, domin ci gaba da hutun karshen shekara a Turai, kafin...

Mafi Shahara