DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu za ta yanke hukunci kan belin Abubakar Malami a ranar 7 ga Janairu

-

Kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta sanya 7 ga Janairu domin yanke hukunci kan bukatar beli da Abubakar Malami, tsohon Antoni-Janar na Tarayya kuma Ministan Shari’a, ya gabatar bisa zargin safarar kudi.

A halin yanzu, Malami na tsare a gidan gyara hali na Kuje tare da dansa, Abdulaziz Malami, da daya daga cikin matansa, Bashir Asabe, wadanda ke fuskantar shari’a a gaban kotu.

Google search engine

Hukumar EFCC ta shigar da tuhume-tuhume 16 a kansu, tana zarginsu da safarar kudade har Naira biliyan 8.7. Dukkaninsu sun musanta zargin lokacin da aka gurfanar da su a ranar 29 ga Disambar 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

EFCC ta yi watsi da zargin Gwamna Bala Mohammed na tsangwamar jami’an gwamnatinsa

Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa tu'annati a Nijeriya ta yi watsi da ikirarin da Bala Mohammed, Gwamnan Jihar Bauchi, ya yi...

Sojoji sun dakile harin ‘yan bindiga a wasu kauyukan Kano

Rundunar sojin Nieriya ta ce ta dakile yunkurin harin ‘yan bindiga da suka yi kokarin shiga wasu al’ummomi a Shanono na Jihar Kano, bayan gumurzu...

Mafi Shahara