DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin Rivers na shirin tsige Gwamnan jihar

-

Majalisar Dokokin jihar Rivers ta fara shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara tare da mataimakiyarsa Ngozi Oduh, bisa zargin aikata manyan laifuka da saba wa kundin tsarin mulkin ƙasa.

Rahotanni sun nuna cewa a zaman majalisar da aka yi ranar Alhamis, 8 ga Janairu, 2026, wanda aka watsa kai tsaye ta gidan talabiji na Channels,wanda Shugaban Majalisa Martins Amaewhule, ya jagoranta, Shugaban masu rinjaye, Hon. Major Jack, ya karanta takardar zarge-zarge da manyan laifuka da ake yi wa Gwamna Fubara.

Google search engine

‘Yan majalisa 26 ne suka sanya hannu kan takardar, inda suka ce zarge-zargen sun shafi saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Shugaban majalisar, Amaewhule, ya ce za a miƙa wa Gwamna Fubara takardar sanarwar zarge-zargen cikin kwanaki bakwai masu zuwa, kamar yadda doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed

Dangote ya janye korafin zarge-zargen cin hanci da ya shigar a hukumar ICPC kan Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMMPRA Jaridar Daily Trust ta ce attajirin...

Nijeriya na bin kasashen Nijar, Togo da Benin tulin bashin kudin lantarkin da ya kai N25bn – NERC

Hukumar kula da lantarki ta Nijeriya NERC ta ce, kasar na bin kasashen Togo, Nijar da Benin bashin dala $17.8m — kimanin N25bn na lantarkin...

Mafi Shahara