DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Majalisar dokokin Kano sun goyi bayan shirin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ficewa daga NNPP zuwa APC

-

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bayyana goyon bayanta ga shirin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ficewa daga jam’iyyar NNPP, tana mai cewa rikicin shugabanci da shari’o’in kotu da ke addabar jam’iyyar na iya jefa kujerarsa cikin barazana.

Shugaban masu rinjaye na Majalisar, Hon. Lawan Hussaini, ne ya bayyana hakan lokacin da yake ganawa da manema labarai a Kano ranar Alhamis, inda ya ce ci gaba da zama a NNPP ya zama hadari ba ga gwamna kaɗai ba, har da sauran zababbun jami’an gwamnati a jihar.

Google search engine

Daily Trust ta rawaito Hussaini, na cewa NNPP na fama da rarrabuwar kawuna a shugabanci da kuma tarin shari’o’in kotu, lamarin da ke janyo rashin tabbas kan sahihancin tsarin jam’iyyar da tsayar da ’yan takara a zabuka masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar...

Shugaba Trump na Amurka ya amince cewa ba Kiristoci ne kadai ake halakawa a Nijeriya ba

Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda...

Mafi Shahara