DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Majalisar dokokin Kano sun goyi bayan shirin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ficewa daga NNPP zuwa APC

-

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bayyana goyon bayanta ga shirin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ficewa daga jam’iyyar NNPP, tana mai cewa rikicin shugabanci da shari’o’in kotu da ke addabar jam’iyyar na iya jefa kujerarsa cikin barazana.

Shugaban masu rinjaye na Majalisar, Hon. Lawan Hussaini, ne ya bayyana hakan lokacin da yake ganawa da manema labarai a Kano ranar Alhamis, inda ya ce ci gaba da zama a NNPP ya zama hadari ba ga gwamna kaɗai ba, har da sauran zababbun jami’an gwamnati a jihar.

Google search engine

Daily Trust ta rawaito Hussaini, na cewa NNPP na fama da rarrabuwar kawuna a shugabanci da kuma tarin shari’o’in kotu, lamarin da ke janyo rashin tabbas kan sahihancin tsarin jam’iyyar da tsayar da ’yan takara a zabuka masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara