DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za a yi zabukan ‘yan majalisar dokoki da kananan hukumomi a Benin

-

Kasar Benin Republic za ta gudanar da zaɓukan ’yan majalisar dokoki da na ƙananan hukumomi a ranar Lahadi, wata guda bayan wani yunkurin juyin mulki da ya girgiza ƙasar, zaɓen da ake ganin zai yi tasiri kan zaɓen shugaban ƙasa da aka shirya yi a watan Afrilu.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya nuna cewa jam’iyyun da ke ƙarƙashin hadakar shugaban ƙasa, Patrice Talon, na dab da ƙarfafa ikonsu, musamman ganin yadda babbar jam’iyyar adawa ta Democrats ba za ta shiga zaɓukan ƙananan hukumomi ba, kuma an hana ta shiga zaɓen shugaban ƙasa saboda rashin cika sharudda.

Google search engine

A halin yanzu, jam’iyyar Democrats za ta shiga zaɓen majalisa, amma ana fargabar za ta rasa kujeru da dama, kasancewar hadakar jam’iyyar Talon na rike da kujeru 81 cikin 109 na majalisar ƙasar.

Zaɓen na zuwa ne a daidai lokacin da Benin ke fuskantar matsin lamba bayan yunkurin juyin mulki na ranar 7 ga Disamba, wanda sojoji suka dakile cikin sa’o’i tare da taimakon Nijeriya da Faransa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar...

Shugaba Trump na Amurka ya amince cewa ba Kiristoci ne kadai ake halakawa a Nijeriya ba

Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda...

Mafi Shahara