DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya shiga tsakani a rikicin Wike da Fubara

-

Alamu na nuna cewa Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya shiga tsakani a rikicin siyasa da ke gudana tsakanin Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike. Wata babbar majiyar fadar shugaban kasa ta ce Tinubu ya kira Wike domin tattaunawa kan rikicin, inda ake sa ran za a yi ganawar a wajen Nijeriya.

Rahotanni sun kuma ce Gwamna Fubara ya bar Nijeriya a ranar Alhamis da nufin ganawa da Tinubu a kasar Faransa. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ’yan majalisar dokokin Jihar Rivers, da ake dangantawa da Wike, suka kaddamar da sabon yunkurin tsige Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu, bisa zargin aikata manyan laifuka.

Google search engine

Majiyar ta shaida ma jaridar Punch cewa shugaba Tinubu ba zai lamunci rikicin ya kara dagulewa ba, musamman ganin barazanar tabarbarewar tsaro da tasirinsa ga arzikin kasa. Ta ce Tinubu na ganin matakin tsige Fubara a wannan lokaci na iya haddasa rikici a yankin Neja Delta, lamarin da ya sa ya dauki matakin shiga tsakani domin dawo da zaman lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara