DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna da cikakken bayani kan harin da Amurka ta kai a Jihar Sokoto amma ba za mu bayyana ba – Rundunar ‘yan sandan Nijeriya

-

Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta ce tana da bayanai kan hare-haren sama da Amurka ta kai kan ’yan ta’adda a Jihar Sakkwato, amma ba za ta fitar da su ga jama’a ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin, ya bayyana hakan a ranar Talata, yana mai cewa batun ya shafi harkar tsaro.

Google search engine

Hundeyin ya ce an yi hadin gwiwa da wasu hukumomi, amma ya dace bangaren tsaron soja ne ya yi karin bayani. Ya jaddada cewa rundunar ’yan sanda ba za ta yi tsokaci kan cikakken aikin ba.

Hare-haren sun gudana ne a ranar 25 ga Disamba, 2025, inda Amurka ta ce ta hallaka ’yan ISIS da dama bisa amincewar gwamnatin Nijeriya.

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce Nijeriya ce ta bayar da bayanan sirri, yana mai jaddada cewa hadin gwiwar na cikin yaki da ta’addanci, ba tare da la’akari da addini ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara