Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta ce tana da bayanai kan hare-haren sama da Amurka ta kai kan ’yan ta’adda a Jihar Sakkwato, amma ba za ta fitar da su ga jama’a ba kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin, ya bayyana hakan a ranar Talata, yana mai cewa batun ya shafi harkar tsaro.
Hundeyin ya ce an yi hadin gwiwa da wasu hukumomi, amma ya dace bangaren tsaron soja ne ya yi karin bayani. Ya jaddada cewa rundunar ’yan sanda ba za ta yi tsokaci kan cikakken aikin ba.
Hare-haren sun gudana ne a ranar 25 ga Disamba, 2025, inda Amurka ta ce ta hallaka ’yan ISIS da dama bisa amincewar gwamnatin Nijeriya.
Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce Nijeriya ce ta bayar da bayanan sirri, yana mai jaddada cewa hadin gwiwar na cikin yaki da ta’addanci, ba tare da la’akari da addini ba.



