DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka za ta kashe $413m kan yaƙi da matsalar tsaro a Nijeriya da Afirka a 2026

-

Gwamnatin Amurka ta ware kusan Naira biliyan 587 domin ayyukan yaki da ta’addanci a Nijeriya da wasu kasashen Afirka a shekarar 2026, sakamakon tabarbarewar tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Kudaden suna cikin Dokar Kasafin Tsaron Amurka ta 2026 (NDAA), wadda ta amince da kashe dala miliyan 413.046 ga rundunar sojin Amurka a Afrika (AFRICOM), kamar yadda takardun da aka samu suka nuna. Dokar ta samu sahalewar Shugaban Amurka, Donald Trump, a ranar 18 ga Disamba, 2025.

Google search engine

Kasafin ya zo ne a lokacin da Nijeriya ke fama da ta’addanci a Arewa maso Gabas, fashin daji a Arewa maso Yamma, da kuma laifukan teku a Tekun Guinea, yayin da kasashen Mali da Benin ke fama da hare-haren ‘yan jihadi daga yankin Sahel.

Dokar ta kuma tanadi kafa ofishin Mataimakin Sakataren Harkokin Afirka a Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, domin sa ido da daidaita manufofin Amurka a Afirka ta Kudu da Sahara, tare da bibiyar tasirin dabarun soja na Rasha a nahiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara