DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka za ta kashe $413m kan yaƙi da matsalar tsaro a Nijeriya da Afirka a 2026

-

Gwamnatin Amurka ta ware kusan Naira biliyan 587 domin ayyukan yaki da ta’addanci a Nijeriya da wasu kasashen Afirka a shekarar 2026, sakamakon tabarbarewar tsaro a yankin Yammacin Afirka.

Kudaden suna cikin Dokar Kasafin Tsaron Amurka ta 2026 (NDAA), wadda ta amince da kashe dala miliyan 413.046 ga rundunar sojin Amurka a Afrika (AFRICOM), kamar yadda takardun da aka samu suka nuna. Dokar ta samu sahalewar Shugaban Amurka, Donald Trump, a ranar 18 ga Disamba, 2025.

Google search engine

Kasafin ya zo ne a lokacin da Nijeriya ke fama da ta’addanci a Arewa maso Gabas, fashin daji a Arewa maso Yamma, da kuma laifukan teku a Tekun Guinea, yayin da kasashen Mali da Benin ke fama da hare-haren ‘yan jihadi daga yankin Sahel.

Dokar ta kuma tanadi kafa ofishin Mataimakin Sakataren Harkokin Afirka a Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, domin sa ido da daidaita manufofin Amurka a Afirka ta Kudu da Sahara, tare da bibiyar tasirin dabarun soja na Rasha a nahiyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara