DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta gargadi jihohi kan yin sulhu da ‘yan bindigar daji

-

Gwamnatin Nijeriya ta gargadi gwamnatocin jihohi da kada su shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, tana mai cewa irin wannan sulhu yaudara ce kuma na kara tabarbarewar tsaro.

Ministan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa (ritaya), ya bayyana haka a wata hira da BBC Hausa inda ya ce an taba gargadin Jihar Katsina kan irin wadannan shirye-shiryen, yana mai jan hankalin al’umma da su daina duk wata mu’amala da ’yan bindiga, ciki har da sayar musu da abinci ko kayan bukata.

Google search engine

Ya ce hadin kan jama’a da bayar da sahihin bayanan sirri na da matukar muhimmanci wajen dakile ’yan bindiga kuma duk wanda ya sayar musu da abinci yana cin kudin jini ne.

Ministan ya kuma musanta rade-radin cewa Gwamnatin Nijeriya na biyan kudin fansa, yana mai cewa sojoji na amfani da matsin lamba da bayanan sirri ne wajen ceto wadanda aka sace.

A cewarsa, biyan kudin fansa na kara karfafa aikata laifuka, tare da kira ga iyalai da al’umma su rika kai rahoton sace-sace ga hukumomin tsaro maimakon shiga tattaunawa da masu garkuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara