DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu na shimfiɗa tubalin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa — Minista

-

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Al’umma na Nijeriya, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shimfiɗa tubali mai ƙarfi domin bunƙasar tattalin arziki na dogon lokaci da walwalar al’umma baki ɗaya.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi mambobin ƙungiyar Grassroots Advocacy for Tinubu (GAT) 2027 da suka kai masa ziyarar ban girma a Abuja, kamar yadda wata sanarwa daga Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai, Malam Rabiu Ibrahim, ta nuna.

Alhaji Mohammed Idris ya ce gwamnatin Tinubu ta ɗauki matakai masu tsauri, wasu ma masu wahala, domin daidaita harkokin ƙasa da sanya Nijeriya kan hanya mai ɗorewa ta fuskar tattalin arziki.

Ya ƙara da cewa duk da ƙalubalen da ake fuskanta, alamu na fara bayyana na farfaɗowar tattalin arziki a muhimman fannoni, yana mai jaddada cewa manufofin gwamnatin na nufin samar da ci gaba mai dorewa da romon dimokuraɗiyya ga ’yan Nijeriya gaba ɗaya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara