DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mutanen kauyen da suka sayar da buhunan masara don hada N40m suka biya kudin fansa, aka karbi kudin aka kuma ki sako mutanen a jihar Kaduna

-

Dattawan al’ummar Gidan Waya da ke ƙaramar hukumar Lere a jihar Kaduna sun bayyana cewa sun sayar da buhunan masara sama da 3,000 domin tara Naira miliyan 40 da masu garkuwa da mutane suka nema a matsayin kudin fansa, amma duk da biyan kudin, mutane 13 da aka sace har yanzu na ci gaba da zama a hannun masu garkuwa bayan shafe makonni.

Da yake magana a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kaduna ranar Litinin, Shugaban Kwamitin Dattawa, Malam Rabo Sambo, ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun kai hari al’ummar Gidan Waya ne da tsakar dare a ranar 11 ga Nuwamba, 2025, inda suka kashe mutane hudu, sannan suka yi garkuwa da mutane 13 da suka hada da maza biyar da mata takwas.

Google search engine

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sojoji sun amince an kitsa yunkurin juyin mulki kan Tinubu

Rundunar sojin Najeriya ta amince cewa wasu jami’anta sun kitsa yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne...

Hukumar ‘yansandan Nijeriya ta tsawaita wa’adin daukar jami’ai aiki

Hukumar Kula da ayyukan ‘yansandan Nijeriya (PSC) tare da rundunar ‘yansandan sun tsawaita wa’adin ɗaukar sabbin 'constable' guda 50,000 da makonni biyu, bayan da aka...

Mafi Shahara