DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun amince an kitsa yunkurin juyin mulki kan Tinubu

-

Rundunar sojin Najeriya ta amince cewa wasu jami’anta sun kitsa yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne rahotanni suka bayyana cewa an kama tare da tsare wasu jami’an soja, daga mukamin Kyaftin har zuwa Birgediya Janar, bisa zargin shirya juyin mulki.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Hukumar Leken Asiri (DIA) ce ta gudanar da kamen.

A wancan lokaci, Hedikwatar Tsaro da kuma Fadar Shugaban Ƙasa sun musanta cewa akwai yunkurin juyin mulki, duk da rahotannin da suka danganta lamarin da soke bikin faretin Ranar ‘Yancin Kai ta 1 ga Oktoba da Shugaba Tinubu ya yi.

Sai dai a wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labaran Tsaro, Manjo Janar Samaila Uba, ya fitar, ya tabbatar da cewa kwamitin binciken da aka kafa ya kammala aikinsa tare da miƙa rahoton ga “hukumomin da suka dace”.

Uba ya ce duk jami’an da ake tuhuma, za a gurfanar da su a gaban kotun soja da ta dace, domin fuskantar shari’a bisa tanadin Dokar Rundunar Sojoji da sauran ƙa’idojin aiki da suka dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara