DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnoni na shan suka na rashin taɓuka abin a zo a gani duk da karɓar Tiriliyan 9 daga asusun FAAC a 2025

-

Duk da samun kimanin Naira tiriliyan 9 daga rabon hukumar rarraba kudaden shiga na tarayya (FAAC) a shekarar 2025, gwamnonin jihohi na fuskantar suka daga ƙungiyoyin ƙwadago, ƙungiyoyin fararen hula da jam’iyyun adawa, bisa zargin cewa akwai tazara mai faɗi tsakanin karuwar kudaden shiga da ƙarancin ayyukan jin daɗin jama’a.

Bincike kan bayanan rarraba kudaden Asusun Tarayya da Hukumar Kididdiga ta Ƙasa (NBS) ta wallafa, wanda jaridar The PUNCH ta tattara, ya nuna cewa rabon FAAC ga jihohi ya ƙaru da sama da N2tn cikin shekara guda.

Wannan ya jawo suka daga ƙungiyoyin ƙwadago da jam’iyyun adawa.

Google search engine

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi gargaɗin cewa, duk da ƙarin kudaden da jihohi ke samu, ba a ga canji mai ma’ana a rayuwar jama’a ba, tana danganta hakan da raunin shugabanci, fifiko marar dacewa, da cin hanci da rashawa a matakin jihohi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Trump ya cancanta a bashi lambar yabo ta zaman lafiya ta duniya – FIFA

Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, Gianni Infantino, ya kare matakin da ya dauka na bai wa Shugaban Amurka, Donald Trump, lambar yabo ta...

Amurka za ta kori ’yan Nijeriya 79 da suka aikata manyan laifuka

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida ta Amurka ta bayyana cewa za ta kori ’yan Nijeriya ba ƙasa da 79 da aka yanke wa hukunci bisa aikata...

Mafi Shahara