Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa ba gudu babu ja da baya kan gyare-gyaren tattalin arziƙi, duk da radadin da aka fuskanta a farkon aiwatar da su, yana mai jaddada aniyar ci gaba da aiwatar da wadannan manufofi.
Jaridar Punch ta raiwato Tinubu na bayyana hakan ne a ranar Talata, 4 ga Fabrairu, 2026, lokacin da ya karɓi tawagar Bankin Duniya karkashin jagorancin Anna Bjerde.
A cewarsa, gyare gyaren ciki har da cire tallafin man fetur da gyara farashin canjin kuɗaɗe sun kasance masu wahala da farko, amma sun zama dole domin ƙarfafa tattalin arziƙin Nijeriya, musamman don ƙirƙirar dama ga matasa masu tasowa a kasar.



