Sarkin Kano, Alhaji na 15 Muhammadu Sanusi II, ya ce ba sai kundin tsarin mulki ya ba shi dama kafin ya ba Shugaban kasa ko Gwamna shawara kan muhimman al’amuran da suka shafi ƙasa ba, yana mai jaddada muhimmancin sarakuna wajen gina ƙasa da kyakkyawan shugabanci.
Sarkin ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels Television a ranar Laraba, 4 ga Fabrairu, 2026.
Ya ce ikon ba da shawara yana fitowa ne daga matsayin da yake da shi a matsayin jagoran al’umma, ba wai dole sai doka ta bashi damar ba.
Sarkin ya nanata buƙatar shigar mata a siyasa da harkokin mulki, yana cewa hakan zai ƙara inganta shugabanci da haɗin kai.



