DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan sanda sun dakile yunkurin kai hari a Zamfara, tare da kama masu bai wa ’yan bindiga bayanai

-

Rundunar ’yan sandan jihar Zamfara sun dakile wani yunkurin kai hari da ’yan bindiga suka yi kan titin Gusau–Talata Mafara, inda aka jikkata jami’inta guda ɗaya yayin musayar wuta.

Jaridar The Guardian ta ruwaito cewa tawagar ’yan sanda karkashin jagorancin DSP Ma’aji Ndagunu na dawowa ne daga Gusau, a lokacin da ‘yan bindigar suka yi musu kwanton bauna a kauyen Kwanar Kirya.

Google search engine

’Yan sandan sun mayar da martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa zuwa dazuka, ana zargin wasu sun jikkata da harsasai.

A yayin artabun, Insp. Jamilu Abdullahi ya samu rauni a cinyarsa ta dama, inda aka garzaya da shi Asibitin Talata Mafara domin jinya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jinkirin gyaran Dokar Zabe na iya shafar jadawalin zaben 2027 — INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Nijeriya (INEC) ta ce jinkirin yin gyara ga Dokar Zabe na iya shafar jadawalin gudanar da zaben 2027. Shugaban INEC,...

Ba sai kundin tsarin mulki ya ban dama ba, zan iya bai wa duk wani mai mulki shawara – Sarki Sunusi II

Sarkin Kano, Alhaji na 15 Muhammadu Sanusi II, ya ce ba sai kundin tsarin mulki ya ba shi dama kafin ya ba Shugaban kasa ko...

Mafi Shahara