DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Dokokin Kano ta musanta yunkurin tsige mataimakin gwamna

-

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta karyata rahotannin da ke yawo na cewa ana shirin tsige Mataimakin Gwamnan jihar, Alhaji Aminu Abdulsalam Gwarzo, tana mai bayyana rahotannin a matsayin marasa tushe.

Da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Asabar, mai magana da yawun Kakakin Majalisar, Kamaluddeen Sani Shawai, ya ce babu wata tattaunawa, kudiri ko shiri a cikin Majalisar da ke nufin tsige mataimakin gwamnan.

Ya jaddada cewa rahotannin da wasu kafafen yada labarai ke yadawa ba su da sahihanci, kuma na iya haddasa tashin hankali na siyasa ba tare da wani dalili ba a jihar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara