Majalisar Dattawan Nijeriya ta janye matsayinta na baya tare da amincewa da tura sakamakon zabe ta kai tsaye daga rumfunan zabe zuwa dandalin IReV na INEC, inda ta tanadi cewa idan tsarin yanargizo ya gaza, takardar EC8A za ta zama babbar hanyar tattara sakamako.
Majalisar ta dauki wannan matsaya ne a zaman gaggawa da ta yi a Abuja, bayan amincewa da kudurin da mai tsawatarwa na Majalisar, Sanata Mohammed Monguno, ya gabatar, wanda Shugaban ‘Yan Adawa, Sanata Abba Moro, ya mara wa baya.
Shugaban Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya karanta sabon tanadin Sashe na 60(3) kafin a kada kuri’a, inda mafi yawan sanatoci suka amince da gyaran.
Sanata Monguno ya ce an dauki matakin ne domin dokar zabe ta dace da muradin ‘yan Nijeriya da kuma tabbatar da sahihin zabe mai gaskiya da adalci.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa da farko zaman ya kaure da hayaniya, bayan wasu sanatoci sun nuna rashin jin dadi da wasu kalmomi da ke cikin sabon tanadin, sai dai daga bisani Majalisar ta amince da shi.



