Madugun adawa a Nijeriiya Atiku Abubakar ya mika sakon jajantawa ga ’yan kasuwa da iyalan da suka yi asarar dukiya a kasuwar Singer da ke birnin Kano, inda ya bayyana alhininsa kan asarar da aka yi.
Haka kuma, ya yaba da kokarin da gwamnatin Kano ke yi na daukar matakan gaggawa domin tallafawa wadanda suka yi asara, yana cewa hakan na kara samar da fata a cikin halin kunci.
Sai dai ya bukaci a fadada kokarin domin samar da cikakken tallafi, farfado da sana’o’in da abin ya shafa, tare da daukar tsauraran matakan kariya domin kauce wa sake faruwar irin wannan iftila’i a kasuwanni.



