Hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya , SSS ta ce za ta gurfanar da tsohon gwamnan Kaduna State, Nasir El-Rufai, a gaban kotu ranar 25 ga Fabrairu, bisa zargin aikata laifukan intanet.
Kamfanin dillancin labarai na Nijeri NAN, ya rawaito mai shari’a Joyce Abdulmalik ce ta saka ranar shari’ar bayan babban alkalin kotun tarayya, mai shari’a John Tsoho, ya mika mata shari’ar.
DSS ta shigar da tuhume tuhume uku kan El-Rufai bisa zargin yin kutse a kiran wayar mai ba shugaba Tinubu shawara kan harkar tsaro Nuhu Ribadu.
A wata hira da El-rufa’i ya yi a gidan talabijin na Arise a kwanakin baya, ya ce shi da wasu suna sauraron kiran wayar Nuhu Ribadu abinda wasu ke ganin hakan na barazana ga tsaron kasa.



