DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanata Kingibe ta zargi Wike da tafiyar da mulkin kama-karya a Abuja

-

Sanata mai wakiltar Babban Birnin Tarayya (FCT), Ireti Kingibe, ta zargi Ministan FCT, Nyesom Wike, da tafiyar da mulki irin na kama-karya tare da kin hada kai da masu ruwa da tsaki a yankin.

Da take magana a shirin Politics Today na Channels Television, Kingibe ta ce ministan ba ya son yin aiki tare da zababbun wakilai da jami’an gwamnati domin kai ribar dimokuradiyya ga mazauna FCT.

Google search engine

Ta bayyana cewa duk da wasikun da ta aike masa tana nuna shirinta na ba da hadin kai, har yanzu ba ta samu amsa mai gamsarwa ba.

Har ila yau, Kingibe ta soki matakin da ministan ya dauka na kakaba dokar hana fita ta awanni 22 gabanin zaben kananan hukumomin da ake gudanar wa a ranar 21 ga Fabrairu a Abuja.

Ministan ya ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar hutu tare da hana zirga-zirga daga karfe 8 na dare zuwa 6 na safe washegari Asabar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 99 domin rigakafin cutar mahaukacin kare

Gwamnatin jihar Kano ta amince da kashe Naira miliyan 99 domin fara shirin rigakafin cutar mahaukacin kare (rabies), inda ake sa ran yi wa akalla...

Wike ya koka kan ƙarancin masu fitowa zabe a Abuja

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda ake gudanar da zaɓen kananan hukumomi cikin lumana a fadin Abuja, duk da...

Mafi Shahara