Jami’ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa.
Rahotanni sun ce matakin ya biyo bayan shawarar kwamitin jami’ar da ke binciken laifukan jarrabawa na zangon karatu na biyu na shekarar 2024/2025.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktar harkokin ilimi ta jami’ar, Nora Dannatta ta sanya wa hannu, yayin da daraktan hulda da jama’a na makarantar, Abdullahi Yahaya-Bello, ya fitar da a birnin Dutse.
Sanarwar ta bayyana cewa majalisar jami’ar ta kuma wanke dalibai biyu daga zargin da ake musu, kazalika daliban da aka dau wannan matakin sun fito ne daga ɓangarori daban-daban na jami’ar.



