DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

-

Jami’ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa.

Rahotanni sun ce matakin ya biyo bayan shawarar kwamitin jami’ar da ke binciken laifukan jarrabawa na zangon karatu na biyu na shekarar 2024/2025.

Google search engine

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktar harkokin ilimi ta jami’ar, Nora Dannatta ta sanya wa hannu, yayin da daraktan hulda da jama’a na makarantar, Abdullahi Yahaya-Bello, ya fitar da a birnin Dutse.

Sanarwar ta bayyana cewa majalisar jami’ar ta kuma wanke dalibai biyu daga zargin da ake musu, kazalika daliban da aka dau wannan matakin sun fito ne daga ɓangarori daban-daban na jami’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara