Hukumar tsaron Civil Defence (NSCDC) ta bayyana shirin tura jami’an ta na Agro-Rangers sama da dubu goma sha daya domin kare manoma a fadin Najeriya yayin da ake shirin fara kakar noma ta shekarar 2026.
Mai magana da yawun hukumar, Babawale Afolabi, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da jaridar Sunday Punch, inda ya ce hukumar na daukar matakai masu karfi domin tabbatar da tsaron manoma da kuma kare harkokin noma a kasar.
A cewarsa, shugaban hukumar NSCDC, Abubakar Audi, ya sake jaddada kudurin hukumar na tura jami’an da aka horar musamman zuwa wuraren noma domin kare rayukan manoma da dukiyar da ta shafi noma.
Matakin na zuwa ne bayan jerin hare-hare da suka faru kan manoma a wasu sassan Najeriya a shekarar 2025.



