DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar tsaron Civil Defence za ta tura dakaru 11,000 da za su kare manoma a gonaki

-

Hukumar tsaron Civil Defence (NSCDC) ta bayyana shirin tura jami’an ta na Agro-Rangers sama da dubu goma sha daya domin kare manoma a fadin Najeriya yayin da ake shirin fara kakar noma ta shekarar 2026.

Mai magana da yawun hukumar, Babawale Afolabi, ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da jaridar Sunday Punch, inda ya ce hukumar na daukar matakai masu karfi domin tabbatar da tsaron manoma da kuma kare harkokin noma a kasar.

Google search engine

A cewarsa, shugaban hukumar NSCDC, Abubakar Audi, ya sake jaddada kudurin hukumar na tura jami’an da aka horar musamman zuwa wuraren noma domin kare rayukan manoma da dukiyar da ta shafi noma.

Matakin na zuwa ne bayan jerin hare-hare da suka faru kan manoma a wasu sassan Najeriya a shekarar 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara