DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Birtaniya za ta rufe wasu hanyoyin jiragen sama da kuma tituna, baya ga girke jami’an tsaro don tarbar shugaban Nijeriya Bola Tinubu a mako mai zuwa

-

Mahukunta a Burtaniya sun sanar da tsauraran matakan tsaro a garin Windsor yayin da Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, zai kai ziyara ta musamman a mako mai zuwa bisa gayyatar Sarkin Birtaniya, King Charles III.

‘Yan sandan Thames Valley sun ce za a kara takaita zirga-zirgar jiragen sama a sararin samaniyar Windsor daga karfe 7 na safe zuwa karfe 11:59 na dare a ranar 18 ga Maris, yayin da za a tura jami’an tsaro da suka hada da masu makamai, rundunar doki da jami’an kula da hanyoyi.

Google search engine

Hukumomin sun ce za a kuma yi amfani da na’urorin CCTV, katangar tsaro da sauran matakai domin tabbatar da tsaron ziyarar da za a yi a Windsor Castle, tare da gargadin cewa duk wanda ya karya dokar hana zirga-zirgar jiragen sama zai fuskanci hukunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara