DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwarzon aikin jarida ya cika 67: Tarihin hikima da jagorancin Dan Malikin Lafiya, Yusuf Sarki Muhammad

-

Daga Muhammad Aliyu Mustapha

A yau muna murnar zagayowar ranar haihuwar babban jigo a masana’antar watsa labarai—Alhaji Yusuf Sarki Muhammad, wanda aka fi sani da sarautarsa ta gargajiya, wato Dan Malikin Lafiya.

Google search engine

Yusuf Sarki Muhammad dai shahararren masanin aikin jarida ne, kwararre a fannin sadarwa, kuma ga shi fitaccen jagora abin koyi a harkar jarida ta zamani.

Duk wanda ya san Yusuf Sarki, zai shaida cewa shi tamkar wata “makaranta ce sukutum-da-guda” idan aka yi la’akari hikimarsa da kuma kwarewarsa a aiki.

Ta yin amfani da kamfaninsa, wato: ‘Actuality and Clips’ da ke Kaduna, Dan Malikin Lafiya ya kwashe shekaru yana rainon matasan ‘yan jarida da ma’aikatan kafafen yada labarai, inda yake koya musu dabarun aikin rediyo da talabijin kai har ma da kafafen sada zumunta na zamani.

Irin zurfin da Yusuf Sarki ya yi a harkar watsa labarai da kuma fahimtarsa ga wannan rayuwar ta duniyar sun sa ya zama tamkar wani babban rumbun ilimi ga duk mai kishirwar kwarewa da hidimtawa kasa. Dan Malikin Lafiya ya shahara da kwarewa bakin aiki da jajircewa wajen kiyaye dokokin tsarin aiki, don tsira da mutunci.

Yawancinmu muna cin moriyar sana’o’inmu ne sakamakon tarbiyya da jagorancinsa; ya nuna mana sirin wannan sana’a kuma ya dasa mana kishin aikin. Mu ne wadanda suka fi amfana da yalwar iliminsa, kuma muna alfaharin dorewar wannan gado nasa.

Muna addu’ar Allah Ya ci gaba da ba shi lafiya da arziki da tsawon kwana; Ya kuma ci gaba da kwararo masa albarkarSa ba tare da yankewa ba har abada. Amin!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Ban shirya yin yarjejeniyar sulhu da Iran don kawo karshen yakin da ake yi ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce har yanzu bai shirya yin wata yarjejeniya da Iran domin kawo karshen rikicin da ke kara tsananta tsakanin kasashen...

Mafi Shahara