Uwargidan shugaban Nijeriya Sanata Oluremi Tinubu ta ce nan da shekarar 2026 Nijeriya za ta rika ba wa wasu kasashen bashin kudade.
Oluremi ta bayyana haka ne a Ile-Ife da ke jihar Oyo, yayin bikin karbar sarauta ta Yeye Asiwaju Gbogbo Ile Oodua.
Jaridar Punch ta ruwaito Remi na cewa akwai kyakkyawan fata a gaba, tana mai jinjinawa gwamnatin Bola Tinubu, bisa ga yadda ta ce ta cimma nasarori masu tarin yawa cikin kankanin lokaci.



