Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana marigayi Shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin jagora mai karfin hali cikin natsuwa da kan ladabi, kuma mai kima da mutunci har zuwa karshen rayuwarsa. Ya ce Buhari ya bar suna na gaskiya, rayuwa mai sauki, tare da akidar cewa rike mukamin gwamnati amana ce, ba damar tara dukiya ba.
Shugaba Tinubu ya yi wannan bayani ne a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, yayin kaddamar da littafin From Soldier to Statesman: The Legacy of Muhammadu Buhari.
Shugaban ya bukaci iyalan Buhari su samu kwarin gwiwa da ta’aziyya daga addu’o’in ‘yan Nijeriya, yana mai jaddada cewa sunan Buhari zai ci gaba da zama abin koyi da zaburarwa wajen hidimar kasa.



