DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta kafa kwamitin bincike kan zargin sauya dokokin haraji

-

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya kafa kwamitin wucin-gadi mai mambobi bakwai domin binciken zargin sabani tsakanin kudirin dokokin haraji da Majalisar Tarayya ta amince da su da kuma nau’ukan da aka rattaba hannu a kansu tare da wallafawa a jaridar gwamnati.

Hon. Muktar Aliyu Betara zai jagorancin kwamitin, yayin da sauran mambobin suka hada da tsohon Mataimakin Kakaki, Ahmed Idris Wase, da Sada Soli, James Abiodun Faleke, Fred Agbedi, Babajimi Benson da kuma Iduma Igariwey.

Google search engine

Matakin ya biyo bayan korafin da dan majalisa mai wakiltar Sokoto, Hon. Abdulsammad Dasuki (PDP), ya gabatar inda ya ce dokokin harajin da aka wallafa ba su yi daidai da abin da ‘yan majalisa suka tattauna kuma suka amince da shi ba, lamarin da ya bayyana a matsayin karya tsarin majalisa da kundin tsarin mulki.

Dasuki ya ce bayan kwashe kwanaki yana kwatanta rubuce-rubucen dokokin da aka wallafa da bayanan kuri’u da kuma sigar da Majalisar Wakilai da Majalisar Dattawa suka amince da ita, ya gano bambance-bambance masu yawa, yana mai cewa abin da aka wallafa ba shi ne abin da aka zartas ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara