DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana barayin daji a matsayin ‘yan ta’adda

-

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana masu garkuwa da mutane da kungiyoyin tada kayar baya a matsayin ‘yan ta’adda, mataki da ke nuna tsanantawa a yaki da satar mutane, hare-hare kan manoma, da tashin hankali a al’ummomi.

Wannan sanarwar ta fito daga Ministan Harkokin Labarai, Mohammed Idris, yayin taron manema labarai na karshen shekara an Abuja.

Google search engine

Ministan ya bayyana cewa daga yanzu, duk wanda ke garkuwa da yara, kai hari kan manoma, ko tayar da tarzoma a cikin al’umma za a dauke shi a matsayin dan ta’adda.

Hakazalika ya ce wannan sabon tsari zai karfafa musayar bayanai da hadin gwiwar aiki tsakanin hukumomin tsaro, wanda zai sa daukar mataki ya zama cikin sauri da tasiri.

Idris ya jaddada cewa hadin gwiwar hukumomi ya riga ya haifar da sakamako, inda a shekarar 2025 aka kama wasu daga cikin ‘yan fashi da ake nema a duniya baki daya ta hanyar ayyukan tsaro masu hadaka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara