Gwamnatin Nijeriya ta ayyana masu garkuwa da mutane da kungiyoyin tada kayar baya a matsayin ‘yan ta’adda, mataki da ke nuna tsanantawa a yaki da satar mutane, hare-hare kan manoma, da tashin hankali a al’ummomi.
Wannan sanarwar ta fito daga Ministan Harkokin Labarai, Mohammed Idris, yayin taron manema labarai na karshen shekara an Abuja.
Ministan ya bayyana cewa daga yanzu, duk wanda ke garkuwa da yara, kai hari kan manoma, ko tayar da tarzoma a cikin al’umma za a dauke shi a matsayin dan ta’adda.
Hakazalika ya ce wannan sabon tsari zai karfafa musayar bayanai da hadin gwiwar aiki tsakanin hukumomin tsaro, wanda zai sa daukar mataki ya zama cikin sauri da tasiri.
Idris ya jaddada cewa hadin gwiwar hukumomi ya riga ya haifar da sakamako, inda a shekarar 2025 aka kama wasu daga cikin ‘yan fashi da ake nema a duniya baki daya ta hanyar ayyukan tsaro masu hadaka.



