DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kananan hukumomi sun bukaci a rika biyan kudadensu kai tsaye daga asusun Gwamnatin Tarayya

-

Ƙungiyar Ƙananan Hukumomi ta Nijeriya (ALGON) da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi (NULGE) sun mara wa Shugaban Nijeriya Bola Tinubu baya kan shirin tilasta biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.

Tinubu ya yi gargaɗin cewa zai fitar da umarni na shugaban ƙasa idan gwamnonin jihohi suka ƙi bin hukuncin Kotun Ƙoli.

Google search engine

Kotun Ƙoli a ranar 11 ga Yuli, 2024 ta haramta wa jihohi riƙe ko sarrafa kuɗaɗen ƙananan hukumomi, tare da bayyana tsarin kwamitin rikon ƙwarya a matsayin saɓa wa Kundin Tsarin Mulki. Duk da haka, har yanzu ba a aiwatar da hukuncin gaba ɗaya ba.

Binciken The PUNCH ya nuna cewa jihohi sun cigaba da sarrafa Naira tiriliyan 7.43 na kuɗaɗen ƙananan hukumomi daga Yuli 2024 zuwa Disamba 2025, duk da umarnin biyan kuɗaɗen kai tsaye.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisa wakilai 6 daga Jihar Rivers sun sauya sheka zuwa APC

‘Yan Majalisar Wakilai 6 daga Jihar Rivers sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC, inda suka danganta matakin da rikicin shugabanci da rabuwar kai da...

Jihohin Yobe da Benue ne suka fi samun yawan ‘yan gudun hijira a Nijeriya – NHRC

Hukumar Kare Haƙƙin Dan Adam ta Ƙasa (NHRC) ta bayyana cewa Jihohin Yobe da Benue ne ke kan gaba wajen yawan ‘yan gudun hijira a...

Mafi Shahara