DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu bai sauya Femi Gbajabiamila daga mukamin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa ba – Bayo Onanuga

-

Fadar Shugaban Nijeriya ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Shugaban Ma’aikatansa, Hon. Femi Gbajabiamila, da Sakatarensa, Hakeem Muri-Okunola.

A wata sanarwa da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar 25 ga Disamba, ya ce labarin ƙarya ne tsagwaronsa, inda ya jaddada cewa Gbajabiamila na nan daram a kan muƙaminsa.

Google search engine

Sanarwar ta ƙara da cewa Hakeem Muri-Okunola ma yana nan a matsayinsa na “Principal Private Secretary”, tana mai kira ga ’yan Nijeriya da su yi watsi da labaran bogi, tare da gargaɗin kafafen yaɗa labarai su rika tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take...

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin...

Mafi Shahara