DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umurci hukumar EFCC ta gabatar da kwamshinan kudi na jihar Bauchi ga kotu bisa zargin safarar N4.6bn

-

Kotun Tarayya da ke Abuja ta umurci Hukumar EFCC da ta gabatar da Kwamishinan Kuɗin Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, a ranar 30 ga Disamba domin gurfanar da shi kan zargin safarar kuɗi har Naira biliyan 4.6.

Mai shari’a Emeka Nwite ya bayar da umarnin ne a ranar Laraba, bayan EFCC ta kasa gabatar da Adamu domin karɓar tuhuma karo na biyu a gaban kotu.

Google search engine

EFCC ta zargi Adamu da kamfanin Ayab Agro Products and Freight Company Ltd da haɗa baki wajen safarar N4.65bn tsakanin Yuni da Disamba 2023, lokacin da yake reshen Manajan Polaris Bank a Bauchi, tare da wasu mutane biyu da ake nema ruwa a jallo.

Lauyoyin wanda ake tuhuma sun koka kan ci-gaba da tsare Adamu ba tare da gurfanar da shi ba, suna cewa hakan na shafar ayyukan gwamnati, musamman biyan albashin ma’aikata a jihar, yayin da kotu ta dage sauraron shari’ar zuwa ranar 30 ga Disamba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan majalisar dokoki 6 a Jihar Zamfara sun fice daga PDP zuwa APC

‘Yan Majalisar Dokokin Jihar Zamfara 6 da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki ta APC, suna zargin take...

Shugaba Tinubu bai sauya Femi Gbajabiamila daga mukamin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa ba – Bayo Onanuga

Fadar Shugaban Nijeriya ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya maye gurbin Shugaban Ma’aikatansa, Hon. Femi...

Mafi Shahara