DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin Rivers na shirin tsige Gwamnan jihar

-

Majalisar Dokokin jihar Rivers ta fara shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara tare da mataimakiyarsa Ngozi Oduh, bisa zargin aikata manyan laifuka da saba wa kundin tsarin mulkin ƙasa.

Rahotanni sun nuna cewa a zaman majalisar da aka yi ranar Alhamis, 8 ga Janairu, 2026, wanda aka watsa kai tsaye ta gidan talabiji na Channels,wanda Shugaban Majalisa Martins Amaewhule, ya jagoranta, Shugaban masu rinjaye, Hon. Major Jack, ya karanta takardar zarge-zarge da manyan laifuka da ake yi wa Gwamna Fubara.

Google search engine

‘Yan majalisa 26 ne suka sanya hannu kan takardar, inda suka ce zarge-zargen sun shafi saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Shugaban majalisar, Amaewhule, ya ce za a miƙa wa Gwamna Fubara takardar sanarwar zarge-zargen cikin kwanaki bakwai masu zuwa, kamar yadda doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara