DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin Rivers na shirin tsige Gwamnan jihar

-

Majalisar Dokokin jihar Rivers ta fara shirin tsige Gwamna Siminalayi Fubara tare da mataimakiyarsa Ngozi Oduh, bisa zargin aikata manyan laifuka da saba wa kundin tsarin mulkin ƙasa.

Rahotanni sun nuna cewa a zaman majalisar da aka yi ranar Alhamis, 8 ga Janairu, 2026, wanda aka watsa kai tsaye ta gidan talabiji na Channels,wanda Shugaban Majalisa Martins Amaewhule, ya jagoranta, Shugaban masu rinjaye, Hon. Major Jack, ya karanta takardar zarge-zarge da manyan laifuka da ake yi wa Gwamna Fubara.

Google search engine

‘Yan majalisa 26 ne suka sanya hannu kan takardar, inda suka ce zarge-zargen sun shafi saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Shugaban majalisar, Amaewhule, ya ce za a miƙa wa Gwamna Fubara takardar sanarwar zarge-zargen cikin kwanaki bakwai masu zuwa, kamar yadda doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya nemi hadin kan ‘yan siyasa a Rivers da su dunkule wuri guda su mara wa Tinubu baya a 2027

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya yi kira ga shugabannin siyasa da al’ummomi a jihar Rivers da su ƙara haɗin kai da fahimtar juna domin tabbatar...

Shugaba Trump na Amurka ya amince cewa ba Kiristoci ne kadai ake halakawa a Nijeriya ba

Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda...

Mafi Shahara