Shugaban Amurka, Donald Trump, a karon farko ya amince cewa ba iya Kiristoci ne matsalar tsaro ta shafa ba, Musulmi ma na daga cikin wadanda suke rasa rayukansu a Nijeriya, duk da cewa ya dade yana nuna cewa Kiristoci ne kawai ake kai wa hari a ƙasar.
Trump ya fadi hakan ne a wata hira da jaridar New York Times, inda ya ce ba addini guda daya ne kawai ke fuskantar matsalar tsaro ba, sai dai duk da haka ya dage cewa Kiristoci ne suka fi shan wahala.
Sai dai ya ce hare-haren da aka kai kan wasu wuraren ‘yan ta’adda a ranar Kirsimeti, Amurka na iya sake kai hare-hare idan ana ci gaba da kashe Kiristoci.



