DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Idan Gwamna Abba ya koma APC, shi ne mutum na farko da za mu fara yankar wa katin jam’iyyar – APC a jihar Kano

-

Jam’iyyar APC a jihar Kano ta bayyana cewa tana maraba da Gwamna Abba Kabir Yusuf bayan ficewarsa daga NNPP, tana mai nuna fatan zai sanar da shigarsa jam’iyyar nan ba da jimawa ba. Sakataren APC na jihar, Ibrahim Zakari Sarina, ne ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayoyi kan matakin da gwamnan zai ɗauka na gaba.

Sarina ya ce kodayake gwamnan bai sanar da shigarsa APC a hukumance ba, jam’iyyar na sa ran hakan zai faru, inda ya jaddada cewa ƙofofin APC a buɗe suke gare shi da magoya bayansa. Ya ƙara da cewa wannan ci gaban na ƙara ƙarfi ga jam’iyyar, ganin yadda ake tsammanin gwamnan zai zo tare da zaɓaɓɓun jami’ai da masu riƙe da muƙamai.

Google search engine

Ya kuma bayyana cewa APC ta riga ta ɗauki matakai na musamman domin karɓar gwamnan, inda ta tanadi lambar rajistar e-registration ta musamman mai lamba 001 a mazabarsa ta Chiranci-Diso. A cewarsa, shirin karɓar ba gwamnan kaɗai ya shafa ba, har da mambobin majalisarsa, masu goyon bayansa da dukkan abokan tafiyarsa na siyasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara