Rundunar sojin Nijeriya ta mika wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu rahoton binciken da ta gudanar kan abin da ta bayyana a matsayin rashin ladabi da karya dokokin aikin soja da wasu jami’an soja 16 da ke tsare suka aikata, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Majiyoyi masu ƙarfi daga ɓangaren tsaro da Fadar Shugaban Ƙasa sun tabbatar wa da jaridar cewa an miƙa rahoton ga shugaban ƙasar ne bayan fiye da watanni biyu na tsanantaccen bincike da tambayoyi, wanda Hukumar Leken Asirin Soja ta Ƙasa (Defence Intelligence Agency – DIA) ta gudanar. Rahotanni a baya sun danganta jami’an da ake tsare da zargin hannu a wani yunƙurin juyin mulki.
Wani rahoto da Sahara Reporters ta wallafa a watan Oktoban shekarar da ta gabata ya bayyana cewa an kama tare da tsare wasu jami’an soja, daga matakin Kyaftin har zuwa Birgediya Janar, a hannun Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (DIA), bisa zargin yunƙurin kifar da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
A wancan lokaci, Hedikwatar Tsaro ta kasa (Defence Headquarters) da kuma Fadar Shugaban Ƙasa sun musanta cewa an yi yunƙurin juyin mulki, duk da rahotanni da dama da suka danganta lamarin da soke bikin faretin Ranar Ƴancin Kai ta 1 ga Oktoba da Shugaba Tinubu ya yi.
Da take magana da jaridar Daily Trust, wata majiya da ke da masaniya kan binciken ta ce tuni an miƙa rahoton ga shugaban ƙasa. Majiyar ta ƙara da cewa matakin da shugaban ƙasa zai ɗauka kan rahoton ne zai buɗe ƙofofin ɗaukar ƙarin matakai na gaba.



