DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rikicin masarautar Kano zai kawo ƙarshe – gwamnatin jihar

-

Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa rikicin da ya dabaibaye batun masarautu a jihar zai samu waraka cikin lumana nan ba da jimawa ba.

Kwamishinan yaɗa labarai da Harkokin cikin gida Ibrahim Waiya ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Kano, inda ya ce gwamnati ta ɗauki matakai masu ƙarfi domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali mai ɗorewa.

Google search engine

Waiya ya jaddada cewa gwamnati na shirin tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki, tare da bin doka, mutunta cibiyoyin gargajiya da kuma kare muradun al’ummar Kano baki ɗaya.

Ya buƙaci al’ummar Kano su kwantar da hankalinsu tare da tabbatar da cewa gwamnati na ci gaba da mayar da hankali kan haɗin kai, ci gaba da shugabanci nagari.

Kwamishinan ya ce za su tabbatar da gaskiya da zaman lafiya a jihar kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta tattaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara