DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar likitoci ta ba gwamnatin Abba Gida-Gida sa’o’i 48 kan zargin cin zarafin likita

-

Kungiyar likitocin Nijeriya reshen jihar Kano, ta ba da wa’adi ga gwamnatin jihar da ta gaggauta korar kwamishiniyar jin kai, Amina Abdullahi, sakamakon cin zarafin wata likita.

Google search engine

A wata sanarwa da shugaban Kungiyar, Dr. Abdurrahman Ali da Sakatare, Dr. Ibrahim D. Muhammad suka sanya wa hannu, kungiyar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 1 ga watan Nuwamba a sashin kula da kananan yara na asibitin kwararru na Murtala Muhammad.

A cewar sanarwar, an yi zargin Kwamishinar da mukarrabanta da jami’an tsaro suka ci zarafin likitar. 

Zargin cin zarafin dai ya samo asali ne sakamakon rashin samun magungunan da aka rubuta wa marasa lafiya, yayin da ta ke kula da marasa lafiya sama da 100.

Biyo bayan wannan al’amari, kungiyar Kano ta yi barazanar dakatar da aikin jinya a asibitin kwararru na Murtala Muhammad cikin sa’o’i 48, idan ba a biya musu bukatunsu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mo Salah ya kafa tarihi a Firimiya inda ya zama dan wasa mafi ba da gudummuwar kwallaye a kulob daya

Dan wasan Liverpool, Mohamed Salah, ya karya tarihin mafi yawan gudummawar kwallaye (zura kwallo da bayarwa) da dan wasa ya taba yi wa kungiya daya...

Duk inda dan Nijeriya yake bai da wuyar ganewa saboda izza da kwarin guiwa a tafiyarsa da mu’amalarsa – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce ana iya gane dan Nijeriya a ko’ina cikin duniya, ciki har da London, saboda irin izza da kwarin...

Mafi Shahara