DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya nada Amb Isma’il Abba Yusuf a shugabancin hukumar NAHCON

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya nada Ambasada Ismail Abba Yusuf a matsayin sabon Shugaba hukumar kula da aikin hajji ta kasa, NAHCON.

 

Google search engine

Nada shi na bukatar amincewar Majalisar Dattawa kamar yadda dokar NAHCON ta 2006 ta tanada.

 

A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan yada labarai, Mr Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Bola Tinubu ya aika wasika ga shugaban Majalisar Dattawa Sanata Godswill Akpabio, yana neman majalisar ta tabbatar da nadin cikin gaggawa.

 

Ambasada Ismail Abba Yusuf zai maye gurbin Farfesa Abdullahi Usman wanda ya yi murabus a wannan mako bayan shafe kusan watanni 14 a mukamin.

 

Sanarwar ta bayyana cewa Ambasada Ismail Abba Yusuf gogaggen jami’in diflomasiyya ne, wanda ya taba zama jakadan Nijeriya a kasar Türkiye daga 2021 zuwa 2024. Ana sa ran nadin nasa zai taimaka wajen ci gaba da tafiyar da harkokin aikin Hajji da ayyukan NAHCON.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara