DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Arewa sun nemi ‘yan majalisa da su yi watsi da kudirin sake fasalin haraji da Tinubu zai yi

-

Gwamnan Bauchi/Gwamnan Jigawa/Gwamnan Gombe

Wani sabon rikici ya kunno kai game da batun sake fasalin haraji a gaban Majalisar Dokoki ta Kasa, yayin da gwamnonin Arewa suka fito fili suka yi watsi da wasu shawarwarin, musamman tsarin raba harajin VAT a daya daga cikin kudirorin.

Gwamnonin Arewa dai sun cimma wannan matsaya ne a ranar Litinin bayan wani taro da suka yi a Kaduna dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Uba Sani na jihar Kaduna, Inuwa Yahaya na Gombe, Dauda Lawal Dare na Zamfara, Abdullahi Sule na Nasarawa, Babagana Zulum na Borno, Bala Mohammed na Bauchi, AbdulRahman AbdulRazaq na Kwara, da Ahmadu Umaru Fintiri na Adamawa.

Gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya a lokacin da yake karanta sanarwar daga taron, ya ce kudaden harajin ya saba wa muradun Arewa, ya kuma umurci ‘yan majalisar Arewa da su yi watsi da kudirin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon dan takarar gwamna na jam’iyyar NNPP a Ondo ya fice daga jam’iyyar

Tsohon dan takarar gwamna a jihar Ondo Olugbenga Edema, na jam’iyyar NNPP, ya fice daga jam’iyyar. Edema ya mika wasikar barin jam'iyyar ga shugaban jam'iyyar na...

Sabbin hare-hare a kananan hukumomi hudu na jihar Benue sun yi ajalin mutum 23

Rahotanni na nuni da cewa kalla mutane 23 sun halaka a wasu jerin hare-haren da aka kai a wasu kananan hukumomi hudu na jihar Benue. Daily...

Mafi Shahara