DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya ya kaddamar da kwamitin aiwatar da ‘yan sandan jihohi

-

Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya Tunji Disu, ya kaddamar da kwamitin mutum takwas domin aiwatar da tsarin kafa ’yan sandan jihohi, bayan amincewa da nadinsa a matsayin IGP na 23 a kasar.

Disu ya ce matakin na daga cikin manufofinsa na gyaran aikin ’yan sanda da karfafa tsaro a fadin kasa. An nada Farfesa Olu Ogunsakin a matsayin shugaban kwamitin.

Google search engine

Disu ya jaddada cewa shugabanci nauyi ne, ba mukami ba, yana mai kiran a sanya kwarewa da rikon amana tare da girmama hakkokin bil’adama a dukkanin ayyukan rundunar.

Nadin Disu ya biyo bayan amincewar Hukumar ‘Yan sanda da kuma nadin da Shugaba Tinubu ya yi masa bayan murabus din tsohon IGP, kuma ana sa ran rantsar da shi a hukumance yayin taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara